Posts

Showing posts from August, 2022

Wasu 'yan Najeriya na caccakar ma'aikatan wutar lantarki kan yajin aiki

Image
  Wasu 'yan Najeriya, musamman masu amfani da shafukan sada zumunta, sun harzuka sakamakon matakin da ma'aikatan wutar lantarkin kasar suka dauka na tafiya yajin aiki. Sun fara yajin aikin ne ta hanyar hana shiga da fita a hedikwatar kamfanin dillancin wutar lantarkin na Najeriya TCN a Abuja, babban birnin ƙasar ranar Laraba da safe. Sun kashe makunnan lantarki a ofisoshin da ke faɗin ƙasar, domin bijire wa umarnin da hukumar da ke sanya ido kan harkokin wutar lantarki ta bayar ga wasu shugabannin riko domin yin jarrabawar karin girma. A watan sanarwa da Sakatare Janar na kungiyar ma'aikatan wutar lantarki, Mista Joe Ajaero ya sanya wa hannu ya umarci dukkan ma'aikatan wutar lantarki su yi zanga-zanga a hedikwatar ma'aikatar wutar lantarki da rassanta da ke fadin kasar saboda umarnin cewa dole su yi "jarrabawar karin girma." Ma'aikatan kamfanin dillancin lantarkin na son a dakatar da tsarin aikin da ake bi na ci gaban ma'aikata. Mista Ajaero ya kar...

Matar da za a ka ɗaure shekara 34 saboda sukar gwamnatin Saudiyya

Image
  Jami'ar Leeds da ke Saudiya ta bayyana damuwa kan yadda aka yanke wa ɗaya daga cikin ɗalibanta da ke digiri na uku hukuncin ɗaurin shekara 34 a gidan yari saboda wallafa wasu saƙonnin Twiter da a ciki ta zagii gwmanatin Saudiyya. An cafke Salma al-Shehab, mai shekara 34 wadda take karatu a jami'ar leeds ta saudiya, wadda ƴar Saudiyya ce kuma tana da yara biyu a 2021 a lokacin da take hutu a ƙasar. Kafin zuwa hutun, ta nemi a samar da sauye-sauye a kuma saki wasu masu fafutuka da ke daure a kurkukun Saudiyya. Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama sun ce hukuncin mai tsauri ya nuna shakku kan iƙirarin Saudiyya na inganta haƙƙin mata kuma ya nuna yadda lamarin ke ƙara lalacewa. Wata kotu da ke hukunta laifukan ta'addanci ta samu Shebab da laifin taimaka wa ƴan adawa wajen ta da hargitsi da yaɗa jita-jita, a cewar ƙungigoyin. Sun ce shi ne hukunci mafi yawa da aka taɓa yanke wa wani mai fafutuka a ƙasar da ke yankin Gulf inda Yarima Mohammed Ibn Salman ke sa ido kan murƙushe ƴan a...

Rashin ƴan takarar Kujerar Sanata na APC a Yobe da Akwa Ibom ...

  Sanata kuma shugaban APC Abdullahi Adamu ya ce ko kaɗan Jam'iyyarsu ta APC ba za ta sake ta yi asarar takarar sanata a mazaɓar Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta arewa-maso-yamma ba, inda hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasar INEC ta ce APC ba ta da ƴan takara. Ya ce ba zai yi tsokaci kan batun ba saboda yana gaban kotu. A makon jiya ne INEC ta bayyana cewa APC ba ta da masu takarar Sanata a mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma. A cewar INEC, APC ta dora sunayen Sanata Ahmad Lawan da Godswill Akpabio cikin jerin sunayen 'yan takara a shafin intanet na INEC sai dai hukumar zaben ta yanke cewa mutanen biyu ba su aka tsayar ba a zaben fitar da gwanin Jam'iyyar.

Rigima kan ƴan takara Musulmai

 Tsohon  Sanata Abdullahi Adamu ya ce batun haɗa ƴan takarar shugaban ƙasa da mataimaki duka Musulmai abu ne da yake ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce sai dai ya ce suna fatan ƙara ƙaimi wajen janyo ra'ayin ƴan ƙasar ga amincewa da wannan zaɓi. Ya ce zai yi wuya a iya shawo kan al'ummar ƙasar kan wannan haɗi saboda "an samu wani hali ne a ƙasar da ko me ka ce, akwai waɗanda suka lashi takobin ba za su yarda ba kuma ba yadda ka iya da su" amma tun da ana kan tsarin dimokraɗiyya ne, kowa yana da ikon ya riƙe ra'ayinsa. APC: Shugaban jam'iyyar Abdullahi Adamu ya ce ya ɗauki alhakin matsalolin da ta shiga Taƙaddama tsakanin CAN da limaman Kirista kan halartar taron APC Ya bayyana cewa Ubangiji ne kaɗai ya san abin da ya sa mutane da dama suka yarda a zuciyarsu cewa haɗin Musulmi da Musulmi shi ne alheri a halin da ƙasar ke ciki. Shugaban na jam'iyyar APC ya ce abu ne mai wahala ka iya samun goyon bayan jama'a ɗari bisa ɗari kan wani ƙudiri a don haka abin da za...

Jam'iyar APC ce za ta ci zaben 2023 duk da matsalar tsaro a Najeriya - Abdullahi Adamu

Image
  Shugaban Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ya ce suna da tabbacin samun nasara a babban zaɓen 2023 mai zuwa duk da tarin ƙalubalen da ƙasar ke ciki musamman matsalar tsaro da tsadan rayuwa.  Tsohon Sanata kuma shugaban jam'iyar APC Abdullahi Adamu ya shaida wa BBC cewa irin waɗannan matsalolin, musamman rashin tsaro, ba kawai a Najeriya ake fuskantar su ba har ma da wasu ƙasashen  duniya. Ya bayyana cewa "Ba shakka akwai lalacewar tattalin arziki a ƙasa, amma mai hankali ya san cewa lalacewar darajar naira ba wai mu muka haddasa ta a nan ba, batun rashin tsaro kuma babu wata ƙasa da za ka ce tana zaman lafiya." Najeriya dai ta shafe tsawon shekaru tana fama da ƙaruwar matsalolin rashin tsaro a sassan ƙasar. A cewarsa, Jam'iyyar APC na aiki ne domin samun nasara a zaɓen da ke tafe sai dai ya ce akwai mutanen da ba ƴan jam'iyyarsu ba da suke musu zagon ƙasa kan wannan ƙudirin nasu. Sai dai ya ce duk da haka gwamnati na kokarin na ganin an magance matsalolin.

Buhari ya sake naɗa Bashir Ahmad mataimaki na musamman

Image
  Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya kuma Kara naɗa tsohon mai ba shi shawara, Bashir Ahmad, a matsayin mataimaki na musamman kan kafofin sadarwa na zamani. Kamfanin yada labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha ne ya tabbatar da naɗin cikin wata wasiƙa da ya aika wa Bashir mai kwanan wata 20 ga Yuli. A cikin wasiƙar, Mr Mustapha ya ce naɗin ya fara aiki ne tun ranar 19 ga watan na Yuli. Bashir ya sauka daga muƙaminsa na mai ba wa shugaban ƙasa shawara sakamakon umarnin da fadar gwamnatin ta bai wa masu son neman takara a zaɓen 2023 da su ajiye muƙaman nasu. Sai dai matashin ɗan asalin Jihar Kano ya yi rashin nasara a zaɓen fitar da gwani a ƙarƙashin jam'iyyarsu ta APC mai mulkin Najeriya, inda ya nemi takararar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Gaya/Ajingi/Albasu daga Kano State. Bashir ya ce an yi maguɗi a zaɓen fidda gonin kuma ya bayyana cewa ya kai ƙara kotu don a bi masa haƙƙinsa.

Dan takarar Senator a jam'iyar APC a Jigawa ya rasu

Image
  Tijjani Ibrahim Gaya, dan  APC da ke takarar sanata a Kudu maso Yammacin Jigawa, ya rasu. Ya rasu a  asibiti a China a jiya Asabar. Rahotanni na cewa sai da aka soma kwantar da shi a wani asibiti da ke Abuja bayan gano cewa yana da cutar huhu kafin daga bisani a fitar da shi zuwa China domin samun cikakkiyar kulawa. Watanni uku kenan da marigayin ya lashe primaries fitar da gwani. Gwamna Jigawa, Muhamamdu Badaru Abubakar, ya ce wannan babban rashi ne a garesu a wata sanarwar ta'aziya zuwa ga iyalansa. Marigayin ya taba wakiltar mazabarsa ta Dutse/Kiyawa a majalisar wakilai tsakanin 2011 zuwa 2015.

Zaben A Kenya: Raila Odinga da William Ruto na tafiya kai da kai Rohoto

Image
  A yayin da aka kammala kidaya kusan rabin kuri'un da aka jefa a zaɓen shugabancin ƙasar Kenya, manyan 'yan takarar biyu na tafiya dai dai. Mataimakin shugaban kasa, William Ruto ya ɗan bai wa tsohon firaminista Raila Odinga tazara kasa da - kashi 51 da 48 cikin 100. Shugaban hukumar zaɓe na kasar ya ce tabbas ana samun jira wajen kidaya kuri'un. Sau da dama ana tsayawa da kidaya kuri'a biyo bayan korafe-korafe daga magoya bayan jam'iyyu. A ranar Asabar, magoya bayan Mista Odinga sun farwa wani yankin da jami'an zaɓe ke aiki, tare da zarginsu da cuta. Yayinda su kuma magoya bayan Mista Ruto ke zargin cewa ana coge a harkokin kidaya kuri'u An dai tsaurara tsaro na raba jami'an kwantar da tarzoma a kowanne yanki na kasar. Kawo yanzu dai an tabbatar da gama kidaya kuri'un mazabu 141 cikin 292. Kuma an bai wa kafofin yada labarai bayanai kan sakamakon wucin-gadi na wadannan mazabu, wanda ke nuna 'yan takarar biyu na tafiya kusa kusa.. Kusan sama da ...

An yi nasarar yi wa ƴarinya mai shekara 6 da aka yanke wa al'aura tiyata a bauchi

Image
  Gwamnatin jihar Bauchi a Najeriya ta ce an yi nasara wajen tiyatar da aka yi wa yarinyar nan ƴar shekara shida da wasu suka yanke wa al'aura watanni hudu da suka wuce. Yanzu haka an sallame ta daga asibiti kuma an hada ta da iyayenta kamar yadda hukumomi suka tabbatar wa BBC a ranar Talata. A cikin watan Janairun wannan shekarar nan ne aka kama wasu matasa biyu masu shekaru 19 da 20 a unguwar Gandu ta karamar hukumar Jama'are, da zargin yanke gaban Hauwa'u Ya'u don yin tsafi. Duka shekarun Hauwa'u shida, kuma bayanai sun nuna cewa matasan sun ja ta ne cikin wani kango da ke unguwar suka yi mata wannan aika-aika.   To sai dai bayan tsintar ta da wasu mutane suka yi, an garzaya da ita zuwa wani asibiti, inda daga baya Gwamna Bala Muhammad ya sa aka kai ta asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH, don yi mata aiki. Watanni hudu kenan, sai a ranar Talata wasu hotuna suka fara yawo a shafukan intanet, da suka nuna gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad rungume da ita tana murmu...

Yara 10 da aka yi wa kisan wulakanci a Najeriya

Image
  Hanifa da Aisha da Husnah na daga cikin yaran da aka taɓa yi wa kisan wulakanci a Najeriya. A shekarun nan za a iya cewa an samu ƙaruwar cin zarafin yara ta hanyar muzguna musu da wulaƙanta rayuwarsu da ma kashe su a Kasar. Duk da cewa babu wasu qidayar a hukumance da ke nuna yadda ƙaruwar ke hauhawa, amma abubuwan da suke faruwa a kewayenmu waɗanda kafafen yaɗa labarai ke ruwaito kawai sun isa a kafa hujja cewa yara na fuskantar munanan ƙalubale a wannan zamani. Kama daga yi musu fyaɗe da azabtar da su da yin safarar su da sacewa don neman kuɗin fansa da kuma sace su don sayar wa iyayen da ba sa haihuwa zuwa kashe su a wuraren da yaƙi da rikici ya yi ƙamari da kuma mayar da su ƴan gudun hijira ƙarfi da yaji. Mafi munin abin da suke fuskanta kuma shi ne kisa, musamman ta hanyar yi musu kisan wulakanci. A wasu lokutan kuma ko da sun tsira da ransu a irin harin da aka kai musu, to yaran kan dauwama cikin firgici sakamakon mummunan halin da aka saka su a ciki. Waɗannan shekarun nan ...

Abin da ya sa ake yawan Rigima kan wajen da za a binne shugabannin Afirka

Image
José Eduardo da ya mutu a watan da ya gabata, ya shafe sama shekara 38 a kan mulki kafin ya sauka a 2017. Cikin jerin saqon nin  wasiƙun da muke samu daga 'yan jaridar Afirka, 'yar kasar Ghana Elizabeth Ohene ta yi rubutu game da irin taqaddamar da ake yi kafin binne shugabannin Afirka. Ba  tabbacin ko zan iya ba da wani  zance, amma ni ban taɓa sanin cewa kasancewar mutum shugaban wata ƙasa a Afirka zai iya haddasa rigima a ƙabarinsa ba idan ya mutu. Na yi ta bin rigimar da ake yi game da inda za a binne tsohon Shugaban Ƙasar Angola José Eduardo dos Santos, wanda ya mutu a Sifaniya ranar 8 ga watan Yuli. Shugaban ƙasar mai-ci João Lourenço da kuma mai dakin sa Dos Santos na son a mayar da gawarsa gida don yi mata jana'izar ban-girma a ƙasaitacciyar maƙabarta ta musamman - abin da muke gani na girmamawa ga shugabanni a Ghana. Amma 'yarsa mai suna Welwitschia "Tchizé" na son a yi masa jana'iza a killace kuma a binne shi a wani ƙabari na musamman a Sifaniya ...

Mohammad Abacha ye na son INEC ta tabbatar da takararsa ta gwamna a Kanon Dabo

Image
  Ɗan takarar gwamnan jihar Kano a  jam'iyyar PDP, Mohammed Abacha ya nemi  kotun Tarayya a Kano ta tilastawa hukumar zaɓe ta INEC tabbatar da shi dan takara ne. Abacha ya qi yadda da  hukuncin da ya tabbatar da cewa Sadiq Wali ne  ɗan takarar PDP na Kano. Mohammed Abacha ya ce shi ne ya lashe zaben fitar da gwamni da aka gudanar a ranar 25 ga watan May wanda ya ce INEC ta tura wakilai domin gani da ido, amma sai kuma aka chanza sunansa da Sadiq Wali. Mai neman takarar na son kotu ta hana PDP da shugaban jam'iyyar na Kano gabatar da Wali a babban zaben da ke tafe a 2023. Akwai dai rarabuwar kawuna tsakanin 'ya'yan jam'iyyar PDP da ke da tsagi biyu a Kano. Wannan dalilin ne ya sa bangarorin da ke rikici da juna kowa ya gabatar da na shi zaben fitar da gwanin. Abin da ya kai ga PDP ta samu 'yan takara biyu kafin daga bisani aka tabbatar wa da Sadiq Wali kujerar takara. Sai dai Mohammed Abacha tun daga wannan lokaci ya ke kalubalantar matsayar jam'iyyar da maka...

Manyan 'yan siyasar Nigeria sun soki harin da aka kai wa Salman Rushdie

Manyan 'yan siyasa da masu rubutu a duk duniya sun qalubalanci harin da aka kai wa Salman Rushdie - da yawan su suka ce wannan tamkar hari ne a kan fadan albarkacin bakin sa. Mai kula a kan tsaro na Amurka, Jake Sullivan ya ce abu ne da baiyi dadi dadi ba. Firaministan Burtaniya Boris Johnson ya ce an far wa Salman ne a kan kudurinsa na aiwatar da 'yancinsa wanda kuma ya cancanci a ba shi kariya da kulawa- shi ma shugaban kasan Faransa Emmanuel Macron ya na da irin wannan ra'ayi. Wani mai rubutu dan asalin Burtaniya Ian MacEwan ya ce harin tamkar an kai shi ne a kan 'yancin yin tunani da fadin albarkacin baki.

NLC ta bukaci shugaban Nigeria Muhammadu Buhari ya ƙara al'bashin ma'aikatan Kasar

Image
  Ƙungiyar kwadago ta NLC a Kasar ta nemi federal Government da ta kara albashin ma'aikatan kasar da kashi 50 cikin 100 lura da yanayin tsadar rayuwa. Kungiyar ta mika wannan bukata ga shugaban qasar Muhammadu Buhari ta wasikar da ke dauke da sa hannun shugabanta Ayuba Wabba. Sakon ya yi tuni da cewa gwamnonin su suka yadda da batun janye tallafin man fetur, da kawo batun ritayan ma'aikatan gwamnati a shekara hamsin, da kuma rage kudaden da ake bai wa majaliasa domin aikin wa 'yan qasa. Ƙungiyar ta zargi gwamnoni kan wadannan shawarwari, su na mai cewa duk wanda ya yadda da ra'ayinsu to shi makiyin gwamnati. Kungiyar ta ce akan karin albashi ne abin da ya fi a mayar da hankali a kai, domin a yanzu  shi ne mafi muhimmanci. Masu fafutikar dai na ganin akwai bukatar gwamnati take amfani da yanayin kasa da abubuwan da ke faruwa wajen fayyace salary da samawa 'yan kasar sauki rayuwa.

Wagila: Yadda ake hada bindigogi domin tunkarar 'yan fashin daji a Sokoto

  Da alamu al'ummomin yakunan karkara a sahar arewa maso yammacin Najeriya na ci gaba amsa kiran da wasu mahukunta suka yi na su yi tattalin makamai domin kare kansu daga harin ‘yan bindiga saboda yadda abin ke wuce gona da iri. A yayin wata ziyara da ya kai a wasu yankuna a jihar Sakkwato kwanakin baya, maaikacin bbc hausa Haruna Shehu – Tangaza ya lura da yadda mutane musamman ‘yan banga ke tanadar wata naui na bindigar gargajiya mai hadarin gaske da ake kira "wagila" domin kare yankunan su. Kan haka ne ma ya samu zantawa da daya daga cikinsu wanda ya fi son a bayyana shi da kawai Sarkin Bindiga yayin da shi ma ya samo tasa wagilar.

Abu biyar da za a iya sa yara su yi a lokacin hutun makaranta madadin zaman banza

Image
  Daga Sadiqa Bkeke A yayin da makarantun firamare da sakandari ke shiga watan dogon hutu, abin da ke damun iyaye shi ne yadda ‘ya’yansu za su amfana da wannan hutun ba tare da zaman banza ba. Masu bincike sun bayyana matakan da suka kamata iyaye su dauka a irin wannan lokaci domin ganin ‘ya’yansu sun mori hutun. Mamu Alhaji Muhammad, mai makarantar firamare ce da ke Abuja, kuma ya yi mana bayani a kan abubuwa da iyaye za su iya taimaka wa yaransu ba tare da dogon nazari ba. Daga cikin abubuwan da ya yi nazari a kai akwai Manhajar koyon karatu Akwai karantarwa ta hanyar manhajoji da ake kira ‘Adaptive Learning System’, inda iyaye za su iya amfani manhajar a wayoyinsu ko kwamfutar hannu da yin rajista. Daya daga cikin manhajojin akwai ‘Youlesson’. YouLeason : Wata manhaja ce da iyaye za su iya saukewa a wayoyinsu ko a kwamfutar hannu ko kwamfutar tebur. Sai su yi rajistar yaransu inda za a ba wa ko wane yaro damar koyon darasi daga wurin malami kai-tsaye ta hanyar bidiyo, yaro na ka...